NIGERUA POLICE

Asalin hoton, NIGERUA POLICE

Rundunar ƴansandan Najeriya ta tunatar da al’ummar ƙasar cewa mutanen da suka ƙi taimakon jami’anta a lokacin da suke neman ɗauki, na iya fuskantar hukuncin ɗauri ko kuma tara.

A cikin wani bayani da rundunar ta wallafa a shafinta na X, rundunar ta ce wannan na ƙunshe ne a sashe na 99 na dokar ƴansanda ta ƙasar ta shekarar 2000.

“Duk wanda aka kira domin ya taimaka wa jami’in ɗansanda wanda – a sa’ilin gudanar da aikinsa ke fuskantar cin zarafi ko hantara ko turjiya – sai mutum ya ƙi, ko kuma ya yi watsi da buƙatar taimakawa, to wannan mutum ya aikata laifi, wanda zai iya janyo a yanke masa tarar naira 100,000 ko ɗaurin wata uku, ko kuma duka biyun idan aka same shi da laifi,” kamar yadda bayanin ya nuna.

Post Views: 6

By Ibrahim