Gwamnatin Kano ta fara kwashe ‘dubban’ yara da ke rayuwa a kasuwanni da ƙasan gadoji a Kano, babban birnin jihar. An fara ɗaukar matakin ne a jiya Litinin, inda aka samar da wani sansanin ajiyewa da kuma tantance yaran.

Shugaban hukumar Hisbah a jihar, Sheikh Aminu Daurawa, ya ce “mun samu rahoton akwai ɗaruruwa ko kuma dubban ƙananan yara da ba su haura shekara 15 ba waɗanda suke kwana a ƙarƙashin gadoji da cikin tashoshi da kuma kasuwanni.”

“Ci gaba da rayuwarsa a waɗannan wurare zai iya haifar da matsala ta tsaro da ta zamantakewa a nan gaba,” in ji Daurawa.

Shugaban na hukumar Hizba ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa akwai irin waɗannan yara masu gararamba a kan tituna sama da 5000. An tsara cewa yaran da aka kwashe za a tara su a wata cibiya, inda za a tantance su, sannan a san matakan da za a ɗauka.

Kano na daga cikin jihohin da ke da yawan al’umma a arewacin Najeriya, kuma ɗaya daga cikin waɗanda ke da yawan ƙananan yara waɗanda ba su zuwa makaranta.

Yaran da Hisbah ta ajiye
Yaran da Hisbah ta ajiye a sansanin alhazai na jihar Kano

Ko da yake jihar na daga cikin waɗanda suka sanya hannu kan dokar kare hakkin yara a Najeriya, har yanzu akwai dubban yara da ke tallace-tallace ba tare da zuwa makaranta ba, yayin da wasu yaran kuma ke barace-barace a kan tituna da sunan neman ilimin addini.

Sheikh Daurawa ya ce bayan kammala tantance yaran, zasu sanya wasu daga cikinsu makaranta yayin da za a koya wa wasu sana’a. Hakanan ya bayyana cewa akwai yiwuwar gurfanar da wasu iyayen da aka tsinci yaran nasu na gararamba kan titi a gaban kotu. “Wanda ya yi sakaci ya bar ɗansa yana yawo a kan titi duk da cewa yana da halin ɗaukar nauyinsa, to za mu gurfanar da shi a gaban kotu”.

Yaran da ba su da iyaye ko waɗanda rikici ya tarwatsa – gwamnatin za ta ɗauki matakin gyara musu rayuwa ta hanyar ba su ilimi da koya musu sana’a.

By Ibrahim